DU'A'UL KUMAIL



DU'A'UL KUMAIL

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI

GABATARWA

Addu'a hanya ce ta ganawa da Ubangiji kai tsaye batare da tsani ba. Allah Ta'ala Ya yi alkawarin amsa wa duk wanda ya kiraye Shi ya roke Shi; sawa'un ya ga amsawar da za a yi masa a nan duniya ko kuma an ajiye masa ita sai a lahira, mai addu'a ba ya daga hannu ya yi addu'a hannunsa ya koma banza. Addu'a makamin mumini ce, da ita ne Allah ke korar babban abokin gabar Bil Adama, wato shedan daga zuciyar mai addu'a ya sanya rundunar alherin da ke cikin zuciya ta yi galaba a kan shedan da rundunarsa. Addu'a garkuwa ce da Allah Ta'ala kan kare mai addu'a daga bala'in duniya da lahira. Da addu'a ne mutum kanji dadin da ke cikin zance da Allah da samun natsuwar kusanci da Shi. Wannan shi ne abinda ya sa Annabawa da Imamai da salihan bayi kan yi riko da addu'a da muhimmancin da bai gaza na ayyukan wajibi ba. Sun yi a aikace, sun koyar sun kuma yi wasici da a yi riko da ita.

"Du'a'ul Kumail" wato addu'ar Kumail addu'a ce mashahuriya wadda ainihinta addu'a ce ta Hidhir (a.s) na zamanin Annabi Musa (a.s) kamar yadda Allama Majlisi ya bayyana, Amirul Mumini Aliyu Bin Abi Talib (a.s) shi ne ya koyar da ita ga Kumail Bin Ziyad, daya daga cikin kebabbun sahabbansa wanda a halin yanzu kabarinsa ke Najaf a Iraki. Ya kasance yana karanta ta a daren rabin watan Saha'aban, da kuma daren Juma'a.

بسم الله الرحمن الرحيم

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai.

اللّهُمّّ إنِّي أسألك بِرَحمَتِكَ الّتي وَسِعَتْ كُلَّ شَيءٍ

Allahumma Inni As'aluka Birahmatikal lati wasi'at kulla shai'in

Ya Allah ni ina rokon Ka da rahamarKa wacce ta game kome da kome,

وَبِقُوَّتِكَ الَّتي قَهَرتَ بِها كُلَّ شيءٍ وخَضَعَ لَها كُلُّ شيءٍ وَذّلَّ لَها كُلُّ شيءٍ



1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 next