Tattaunawa Ta Bakwai



Kun sanya Annabi (s.a.w) yana koyon tauhidi wurin kirista. Kun sanya Annabi yana samun galaba daga shedan da hatta da a sakonsa sai ya gafala ya yabi gumaka maimakon kushe su. Kun sanya Annabi (s.a.w) kasan darajar sauran annabawa. Kun sanya Annabi (s.a.w) yana fushi da kausasawa har ya la'ani wasu mutane ba bisa hakkinsu ba.

Kun sanya Annabi (s.a.w) bai san yadda ake auren dabino ba har shukar mutane ta lalace. Kun sanya Annabi (s.a.w) yana zalunta 'yan Badar ya kama ribatattun babu hakki kuma ya karbi fidiya babu hakki. Kun sanya Annabi (s.a.w) yana fitsari a tsaye a Bolar mutane. Kun sanya yana kuskure da yawa har sai Umar ya gyara masa.

Kun sanya shi shedan yana iya hana shi sallarsa ta dare. Kun sanya shi yana tsere da matarsa a cikin rundunar yaki a sahara. Kun sanya shi yana hana abu shi kuma ya yi. Kun sanya shi yana zuwa kallon rawar 'yan matan Afurka a masallacinsa. Kun sanya shi yana yin alwala da giyar dabino. Kun sanya shi yana samun shagaltuwa da rafkanwa a zuciya har sai ya manta ko ya yi salla ko kuwa, ya zo matansa ko kuwa! Kun sanya shi ana iya yi masa tsafi ya kama shi har ya yi wata shida bai san me yake yi ba!

 Ina tambayarka don Allah ba wannan munanan tubaru da ta cikinsa kuke ganin Annabi (s.a.w) wanda har kuka sanya duniyar yamma ta fake da wadannan abubuwan tana cin mutuncinsa! Ina musulunci zai yi izza!

(Mahallin kuka) Kun sanya shi yana zo wa matansa tara a rana daya, yana zo masu suna haila, yana yin abin da bai dace ba sai ya yi bawali a tsaye, ya karbi baki yana rigingine, ya saurari waka, ya kalli rawa, ya sha Nabiz (giyar dabino)! Ya shagaltu da matarsa A'isha, ya fifita ta a kan sauran matansa, ya saurari kida da waka tare da ita, ya dora ta kan kafadarsa domin su yi kallo ta taga kumatunsa a kan nata domin kallon rawar matan Afrika, ya bar rundunarsa ta yaki ya yi tsere da ita. Kai tsarki ya tabbata ga Allah da annabinsa daga abin da suke siffantawa.

Shi ya sanya wanda yake yi wa Annabi wannan kallon zai ga bai yi wasiyya ba domin ya rena hankalin Annabi (s.a.w) ta yadda ya yi umarni da cewa; Kada mumini ya sake ya yi kwana uku bai rubuta wasiyya ba, amma kuka sanya shi ba ya yi. Koda yake kun samu maganarku ta yi karo da juna a lokacin da kuka ce ya zo ya rubuta wasiyyarsa Umar dan Khaddabi ya hana shi ya ce: ba ya cikin hankalinsa!!! Inna lil-Lahi wa'inna ilaihi raji'un!!!

Hafiz Muhammad

Kammala gyarawa

01 /July/ 2009

 



back 1 2 3 4 5 6 7 8