Tattaunawa Ta Bakwai



Tarihu Bagdad: j 8, shafi: 20, alkahira. Sam'ani Naishaburi a Fadha'ilus sahaba: Da Baihaki: da sanadin da ya gabata. Da Allama Akhdab Khawarizimi: a Manakib, shafi: 93. Da Zakha'irul Ukuba: shafi: 67. Da Masnad: Ahmad bn Hambal. Da: Fara'idus Simdain. Da: Dabari. Da: sauransu.

A yanzu akwai wani daga cikinku da isa ya karyata Umar dan Khaddabi wanda shi ya fi ku sanin waye Ali (a.s)!! ko kuwa ba ku gaskata Umar ba sai inda ya yi muku dadi!!! Hada da abin da ya gabata gareka tun baya yayin da Umar ya yi furuci da cewa; bai'ar da aka yi wa Abubakar kuskure ce.

To idan wannan bai'ar kuskure ce; sannan kuma ta Umar dan Khaddabi ta dogara da wasiyyar wanda yake bai'arsa kuskure ce a fadinsa da bakinsa, sannan ta halifa na Uku ta dogara da wannan ta biyun, ke nan ka ga duk bai'ar ta doru bisa kuskure, wannan yana nufin ke nan sai a nemi wanda yi masa bai'a take sahihiya, kuma ba ka isa ba gabas da yamma ka samu wani wanda yake haka duk duniya sai Ali (a.s)!.

Kuma ina hada maka da kalubalen ka kawo wani malami madogara kwara daya rak da ya yi musun wilayar Imam Ali (a.s) in akwai! Kuma wannan bashi ne da ya hau kanka!

Ina iya kawo maka misali daya cikin daruruwa, duba abin da manzon Allah yake gaya wa khalid dan walid yayin da Manzo ya kwabe shi ya hana shi sukan Ali (a.s) yana mai gaya masa shi ne jagoranku bayana, da sauran ruwayoyi masu nuni da wannan:

Duba: Khasa'isun Nisa'i: 24. Da Haisami a Majma'uz Zawa'id: 9/ 127-128. Da Muntaki: a Kanzul Ummal: 6/ 154-155. da Zakha'irul Ukuba, daga Ahmad dan Hambal a manakib: 68. Da Dabarani a tarihinsa: 3/ 17. Da Mustadrak: 3/ 110. Da Sa'alabi a Tafsirinsa a sallar Isra'i. Da Arraudha: 11. Da akwai dubunnai dalilai sai dai tsoron tsawaitawa da karancin lokuta.

Sannan wahayi shi ne ya zo da biyayya ga manzon Allah bayan Ubangiji da kuma Ulul amri kuma Manzo ya yi bayanin su waye ulul amri, sannan Kur'ani ya yi nuni a sababin nuzulinsa da "Innma waliyyukumul Lahu…"; da ta yi nuni da Allah da Manzo (s.a.w) da Imam Ali (a.s): Arriyadhun Nadhira: 2/ 302. Tafsirul manar: 6/ 366. Tafsiru Ibn Kasir: 2/ 113-114, Bairut 1986.

Sannan akwai hadisan manzilarsa da shi kamar Haruna da Musa (a.s) ne, sannan ga hadisud Daar da ayyana shi halifa bayansa tun farkon da'awa, ga Hadisul Gadir da kowa ya yi sheda da shi ittifakan koda kuwa sun yi musun wani bangare na manufarsa ba asalinsa ba, ga su nan masu yawa da ba zasu kirgu ba.

Amma batun gado da kake cewa; Ka sani Fadima Zahara (a.s) tana daga cikin wadanda Allah ya tsarkake daga sabo sabanin masu jayayya da ita, sannan ta kafa musu hujja da Kur'ani cewa ana gadon annabawa (a.s) su kuma sun kawo hadisin aahaad wanda ba ya iya ture Kur'ani mai daraja.

Sannan jayayyar halifa na uku da matan Annabi (a.s) 'ya'yan halifa na farko da na biyu ta yanke hujja yayin da suka nemi nasu gadon bayan tsawon lokaci, yana mai yi musu raddi da cewa ai kuma kun shaida gun iyayenku da ba a gadonsa (don a hana Fadima (a.s) nata) kuka kawo wani bagidajen balaraben kauye Aus dan Hadasan wanda yake yin salla babu tsarkin bawali ya yi muku sheda kan hakan, don haka ku tashi ku ba ni wuri.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 next