Tattaunawa Ta Bakwai



A wurinku duk Allah zai rube ya halaka –wal'iyazu bil-Lah! Sai kawai fuskarsa zata rage. Albani (fatawa albani: shafi: 522, 523) wani abin mamaki Albani ya yi kakkausan suka ga Buhari saboda ya yi tawilin fuska da mulkin Allah (s.w.t). a wannan ayar: "Kulli shai'in halikun illa wajhah" wanda kuwa Ubangijinsa zai halaka gaba daya sai fuska ba dai Ubangijin da ya aiko manzanni ba ne Ubangijinsa! A nan muna iya gani a fili yake cewa: "Kuna hana tawili amma kuna yin sa inda kuka ga dama, kun gwammace ku sanya Allah zai mutu ya halaka ya kare da ku yi tawili, amma saboda gyara makantar Bn Baz kun yi tawilin "Faman kana fi hazihi a'ama, fahuwa fil akhirati a'ama wa'adhallu sabila" domin ku yi kariya daga makantarsa a lahira. Don me ba ku mayar da ayoyin siffofin Allah zuwa ga muhkamata ba, amma kuka mayar da siffofin dan Adam zuwa ga muhkamata kamar "innaha la ta'amal absar…" domin ku yi kariya ga malaminku. Da ya hau kan al'arshi saboda nauyinsa sai da arshi ya yi kara. Wal'iyanzu billah!

Irin wadannan siffofin ne da kuka ba wa su Ka'abu dama da Tamin bn Aus, da Abdullahi bn Salam suka kawo koyarwar kiristanci da yahudanci cikin musulunci, sakamakon kun yi nisa da Alayen Annabi sai kuka fada cikin wadannan tarkuna nasu.

Ya zauna kan al'arshi ya dora kafa daya a kan daya yana mai jingina kan al'arshi ya kishingida sannan daga baya sai nauyinsa ya tsattsaga sammai. (tafsirud Dabari, j 25, shafi: 6).

Allah yana da 'yan yatsu hudu, ko biyar ko shida da sabanin malamanku a kai. Duba daya daga ciki a Buhari, j 5, shafi: 33. da kitabut tauhid, shafi: 225, amma shafin ya yi daidai da wanda Muhammad Salim malamin Azhar ya gyara.

Akidarku ta cewa; ana ganin Allah da idanu kamar wata: Buhari; 1, s: 195. Pop ya soki Kur'ani saboda tsarkake Allah ya goyi bayan akidar wahabiyanci ta sanya shi jiki saboda ta yi daidai da kiristanci. Duba: Littafin Al'uburu ilar Raja' a hirarsa da dan jaridar Italia. Sannan: Ubangijinku saurayi ne mai nadadden gashi dunkulalle.

Babban malam Ayatul-Lahi Kurani Allah ya tsawaita rayuwarsa yana cewa: "Kun ba wa Allah madaukaki gabobi: sau da yawa "yadullahi fauka aidihim" kuka ki tawilinta da cewa lallai dai hannu ne sosai. Amma duk da tsananin kin tawili da kuke yi idan aka zo da wani abu da ranku ba ta so sai ka ga tawili sosai: ga shi manzon Allah yana cewa: "man kuntu maulahu fa Aliyyu maulahu" "Duk wanda nake jagoransa to Aliyyu (a.s) ma jagoransa ne" a nan kam sai ga tayar da jijiyar wuya domin yin tawili iyakacin karfinku".

Sau da yawa malaman Sunna masu kyawon mahanga suka yi musun wadannan abubuwa masu yawa amma ku kuka dage kansu da kariya iyakacin karfinku. Game da Allah zan bar ka hakan, don haka sai ka yi kokarin sanin Allah, idan ka san shi to duk wadancan matsalolin zasu yi maka sauki.

Mummunan abu na biyu shi ne rashin sanin Annabi (s.a.w), wannan lamari ne mai tsananin cin rai, kun siffanta Annabi (s.a.w) da siffofin da yanzu makiya musulunci suke yi mana isgili da su kamar yadda kuka siffanta annabawa (a.s) da siffofi masu aibata su: irin wannan lamari kamar jingina wa Musa (a.s) tafiya tsirara yana bin tufafinsa, da jingina wa Sulaiman shirka da zaluncin kashe dabbobi babu wani hakki ko dalili, da kwacen mata ga Dawud (a.s) wal'iyazu bil-Lah! da sauransu. Sannan kuma kun ba wa fiyayyen halitta siffa kamar haka; Jingina masa shafar shedan sadda aka haife shi: Buhari 4, 94.

Kun jingina wa Annabi kurakurai da Umar dan Khaddabi ke yi masa gyara sai kuwa Allah ya goyi bayansa a kan abin da ya yi wa Annabi (s.a.w).

Kun dauki tawassuli da ziyarar Annabi (s.a.w) shirka. Kun dauki Annabi da rashin kimar da ibn Abdulwahab ya shelanta cewa; shi "Darish" ne, wato dan sakon da kawai ba shi da kima sai kimar sakon kawai. Kun sanya Annabi yana kokwanton annabtarsa har sai da wani kirista ya gaya masa ai kai Annabi ne sannan ya samu nutsuwa, amma wahayi ya sake jinkiri ya sake kokwanto har ya kusa kashe kansa.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 next