Ayyuka da Sakamako 2



Hadisin da duka bangarori guda biyu suka ruwaito yana nuni ne da cewa, yayin da mutum ya mutu littafin ayyukansa zai kulle, sai kawai ta hanyoyi guda uku:

1-Sadakatu jariya

2-Aikin ilimi da mutum ya yi wanda wasu suke amfana da shi.

3-Idan mutum ya haifi dan kwarai wanda zai rika yi masa addu’a.

Don haka mutum zai iya amfana da wasu abubuwa bayan ya mutu ta wadannan hanyoyi guda. Alhalin kuwa amfanuwa da ayyukan wasu bayan mutuwa ba ya daya daga cikin wadannan guda ukkun.

 

Amsa

Wannan hadisi da aka ambata yana magana ne a kan ayyukan da mutum da kansa ya aikata, saboda haka a nan da sauran magana wato idan mutum ya mutu duk wani aiki wanda shi ne da kansa ya yi sanadinsa zai yanke sai abubwa guda uku wadanda aka ambata wadanda su ne zasu dawwama, sakamakon mutuwar mutum ba zasu yanke ba. Saboda haka wannan hadisi ba shi da alaka da ladar da mutum zai samu sakamakon ayyukan wasu da suka yi saboda shi.

Saboda haka wannan hadisi kai tsaye yana magana ne dangane da ayyukan da mutum ya aikata da kansa ne, wadanda duk zasu yanke bayan mutuwarsa, sai kawai wadannan ayyuka guda uku wadanda zai ci gaba da amfana da su. Don haka wannan shi ne batun da ake magana a kansa a cikin wannan hadisi, saboda haka sam ba shi da alaka da abin da mutum zai samu na lada ta fuskar ayyukan wasu.

 



back 1 2 3 4 5 6 next