Surori; Laili zuwa Mutaffifin



إِنَّ الَّذِينَ فَتَنُوا الْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ الْحَرِيقِ

10. Lalle ne wad'anda suka fitini muminai maza da muminai mata, sa'an nan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, kuma suna da azabar gobara.

إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ جَنَّاتٌ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ ذَلِكَ الْفَوْزُ الْكَبِيرُ

11. Lalle ne wad'anda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan k'warai suna da gidajen Aljanna, k'oramu suna gudana daga k'ark'ashinsu, wancan abu fa shi ne rabo babba.

إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

12. Hak'ik'a damk'ar Ubangijinka mai tsanani ce k'warai.

إِنَّهُ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُ

13. Hak'ik'a shi ne Mai k'aga halitta, kuma Ya mayar da ita.

وَهُوَ الْغَفُورُ الْوَدُودُ

14. Kuma Shi ne Mai gafara, Mai bayyana soyayya.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 next